Tuesday, December 9
Shadow

Wata Kungiya ta yi kiran shugaba Tinubu ya dauki Yakubu Dogara a matsayin mataimakinsa a zaben shekarar 2027

Wata Kungiya daga yankin Arewa maso gabas ta yi kiran shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da ya ajiye Kashim Shettima ya dauki Yakubu Dogara a matsayin mataimakinsa a zaben shekarar 2027.

Kungiyar me suna the Coalition of APC Support Groups in the North-East ta bayyana hakane a zaman data gudanar a ranar Litinin a jihar Gombe.

Kungiyar tace Yakubu Dogara ne wanda yafi dacewa ya zama mataimakin shugaban kasa a shekarar 2027.

Tace zata nada wakilai da zasu jagoranci mutane zuwa ganin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu a Abuja dan isar masa da sakonsu.

Karanta Wannan  AIKIN LADA: Yadda Wani Bawan Allah Ya Zube Ruwan Leda (Pure Water) A Gefen Titin Area 11 Dake Abuja Saboda Masu Bukata

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *