Friday, December 5
Shadow

Ya kamata ana bin doka a kasarnan, Masu son hadani fhada da sojoji ne suke rura whutar rikicin amma ni ina girmama sojoji kuma banda matsala dasu>>Inji Wike

Ministan babban birnin tarayya, Abuja, Nyesom Wike ya bayyana cewa, yana girmama sojoji kuma bashi da matsala dasu.

Ya bayyana hakane a yayin da ake ci gaba da takaddama akan Tirka-Tirkar data faru tsakaninsa da sojan ruwa, AM. Yerima wanda ya hanashi shiga wani fili a Abuja.

Wike yace ya je wajanne bayan samun rahoton cewa, an ciwa daya daga cikin ma’ikatansa Zarafi, yace shi kuma ba zai bari a rika ciwa ma’aikatan dake karkashinsa zarafi ba.

Yace idan an kaika wajan gadi a matsayin jami’in tsaro aka ce ka harbi mutum, idan ka kashye mutum kana tunanin doka ba zata yi aiki akanka bane?

Karanta Wannan  Amaryar Rarara Kenan, Malama Sayyada Aisha Humaira A Wajen Liyafar Da Ta Shirya Na Yabon Annabi Muhammad (S.A.W) A Jihar Borno A Jiya Alhamis

Yace bashi da matsala da sojoji da yasan yana da matsala da sojoji akwai inda zai je ya warware matsalar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *