Thursday, June 5
Shadow

Yan fàshì sun hàrbè mafarauta da fararen hula kimanin 19 har làhìrà a Karamar Hukumar Alƙaleri ta Jihar Bauchi

A yayin ziyarar da ya kai wurin, Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Bauchi, Sani-Omolori Aliyu, ya ba da umarnin yin cikakken bincike da kuma tura karin jami’an tsaro yankin.

Mazauna kauyen Mansur sun ce an kashe ’yan farauta guda tara da kuma fararen hula guda goma, kuma an yi jana’izar ’yan bangar a kauyen Mansur kamar yadda addinin Musulunci ya tanada. Amma ’yan sanada da jami’an Ƙaramar Hukumar Alƙaleri ba su ce komai ba kan adadin mamatan ba.

Kakakin ’yan sanda na jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce kwamishinan ya tattauna da masu ruwa da tsaki a yankin, inda ya buƙaci jama’a su kwantar da hankalinsu, su kuma kasance a cikin shiri, tare da bai wa ’yan sanda goyon baya wajen gudanar da binciken su.

Karanta Wannan  Masu zanga-zanga sun je majalisar tarayya suna neman a kori shugaban NNPC Mele Kolo Kyari daga aiki

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *