Friday, July 17
Shadow

‘Yan Najeriya, Ghana, China, da India ne suka bace aka rasa inda suke bayan da suka shiga kasar Canada da cewar sun je yin karatune

Wani rahoto ya bayyana cewa akalla dalibai dubu 50 ne suka bace aka rasa inda suke bayan da suka shiga kasar Canada da sunan yin karatu.

Daiban sun fito ne daga kasashen Duniya daban-daban wa da suka hada da kasar India da dalibai 19,582 suka shiga kasar ta Canada amma suka ki zuwa su yi rijistar fara karatu aka rasa inda suke, me biye mata itace kasar China dake da dalibai 4,279 da suma bayan shiga kasar Canada da sunan karatu suka bace, kasa ta uku itace Najeriya dake da dalibai 3,902 wanda suma sun shiga kasar Canada da sunan yin karatu amma sun bace, kasa ta gaba itace kasar Ghana itama dalibanta sun isa kasar Canada da sunan yin karatu amma suka bace.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Kalli Bidiyon yanda Dambarwa ta barke a majalisa inda wasu sanatoci suka ce a bar Janar Christopher Musa ya wuce amma wasu sukace basu yadda ba sai an masa tambayoyin da suka kamata

Daliban dai sun shiga kasar Canada ne a tsakanin watannin Maris zuwa Afrilu.

Rahoton yace wasu daliban yaudararsu aka yi inda wasu kuma da gangan suka aikata hakan dan su samu shiga kasar ta canada

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *