
‘Yan majakisar Wakilai musamman wadanda suka fito daga jihohin da matsalar tsaro ta yi kamari sun gayawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya dauki mataki akan lokaci ko kuma mutane na Daf da giwa Gwamnatin sa Bore.
‘Yan majalisar sun bayyana takaici kan kasa magance marsalar tsaro a kasar nan duk da kashe makudan kudaden da suka kai Naira Tiriliyan 19.7 akan tsaron a tsakanin shekarun 2015 zuwa 2019.
An fara tattaunawar ne biyo bayan korafin harin da aka kai kan Giwa Barak a jihar ta Borno da kuma kashe-kashen da ake yi a Jihohin Borno da Yobe.
Dan majalisa, Ahmed Satomi ya fara yin maganar a zaman majalisar inda sauran ‘yan majalisar da yawa suka nuna damuwa sa alhini.
Kakakin majalisar, Godswill Akpabio yace ya kamata a bar maganar siyasa a dakatar da wannan matsalar tsarom