
Kakakin majalisar Dattijai, Godswill Akpabio ya jawo hankalin abokan aikinsa Sanatoci kan cewa ‘yan Najeriya na cikin Wahala.
Ya bayyana hakane a cikin jawabinsa na farko bayan komawar majalisar hutun da ta yi.
Yace abinda ya kamata su mayar da hankali akai shine baiwa maganar tsaro, Inganta rayuwar mutane, da bangaren Makamashi.
Yace ya kamata su taimakawa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu wajan kawar da matsalar da wahalar da ‘yan Najeriya suke ciki.
r