Saturday, March 15
Shadow

Ƙungiyar dattawan arewa ta buƙaci a yi bincike kan rikicin Natasha da Akpabio

Ƙungiyar dattawan arewacin Najeriya, wato Arewa Consultative Forum ko kuma ACF a taƙaice ta nuna damuwarta kan zargin cin zarafi da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi ga shugaban majalisar dattawa, Sanata Godswill Akpabio.

A wata sanarwa da ta fitar a ranar Lahadi wanda kakakin ƙungiyar, Muhammad-Baba ya sanya wa hannu, ƙungiyar ta ce akwai buƙatar a gudanar da bincike mai kyau domin tantance sahihancin zargin, kamar yadda tashar Channels a shafinta na intanet.

“A yanzu dai yadda abubuwa suke shi ne zargin nan zai iya ɓata sunan Najeriya a idon duniya,” in ji ƙungiyar, wadda ta nuna damuwa kan yadda a cewarta har zuwa yanzu, sanatocin arewa ne kaɗai suka fuskanci takunkumi kamar dakatarwa a majalisar ta 10.

Karanta Wannan  Wata Sabuwa: Iyalan marigayi Shugaban sojojin, Lagbaja sun yi zargin cewa kasheshi aka yi

“Wannan ya sa ACF ke fargabar ko dai abin ɓoye ne ya fara fitowa fili na yaƙi da yankin arewa. Wannan ya sa muke kira da a kawo ƙarshen wannan lamarin.”

Ƙungiyar ta yi kira da sanatocin arewa su goyi bayan Natasha, sannan ta buƙaci a gudanar da bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *