Saturday, May 31
Shadow

Ƴansanda sun kama matashi kan zargin kashe mahaifinsa a Jigawa

Rundunar ƴansanda a jihar Jigawa ta ce ta kama wani matashi da ake zargi da sassara mahaifinsa har lahira.

Lamarin ya faru ne a safiyar yau Litinin a garin Sara da ke karamar hukumar Gwaram.

Tuni aka yi jana’izar mahaifin matashin – inda shi kuma yake tsare a wajen ƴansanda.

Mai magana da yawun ƴansanda jihar SP Lawan Shi’isu Adam, ya shaida wa BBC cewa jami’ansu sun tarar da mahaifin cikin jini lokacin da suka isa gidansa.

“Yaron ya sassare mahaifin nasa a kafaɗarsa, ya kuma yanka maƙogoronsa har zuwa kirjinsa. Nan da nan aka ɗauke shi zuwa asibiti a Birnin Kudu inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa,” in ji SP Lawan Shi’isu.

Karanta Wannan  Ji Yadda Gwamna Abba Gida-gida ya taimaki dalibar da ke fama da lalura bayan ta tura masa sako na neman taimako

Ya ce an yi ƙoƙarin an kama matashin da kuma addar da ya yi amfani da ita wajen sare mahaifin nasa.

Kakakin ƴansandan ya ƙara da cewa yanzu suna yin bincike domin gano abin da ya sa matashin ya yi wa mahaifinsa irin wannan ɗanyen aiki.

“Matashin yana hannun mu a yanzu kuma muna ci gaba da bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *