Friday, June 26
Shadow

Kalli Hoton matar da kotu ta yankewa hukuncin kis-sa ta hanyar ra-ta-ya a jihar Kebbi saboda kash-she mijinta, saidai tace bata yadda a kash-sheta ba, zata daukaka kara

Babbar Kotu a jihar Kebbi ta yankewa Fatima Abubakar hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samunta da laifin kashe mijinta Attahiru Muhammad-Ibrahim.

Lamarin ya farune a ranar 25 ga watan Augusta na shekarar 2022 inda Fatima ta cakawa mijin nata wuka a ciki.

Mai shari’a, Justice Umar Abubakar ne ya yanke wannan hukunci inda yace sun samu hujjoji masu karfi dake nuna cewa lallai Fatima ce ta kashe mijinta.

Yace kuma an yanke mata hukuncin daurin shekaru 7 a gidan yari saboda azabtar da mijin nata da ta yi.

Saidai lauyan Fatima, Sani yace zasu daukaka kara.

Karanta Wannan  Sadiya Haruna Ta Grime Ni, Shekaru Na 35 Ita Kuma Shekarunta 48, Kuma Kafin Mu Rabu Na Ba Ta Hakuri Ya Fi Sau Milyan Duk Da Cewa Ita Ta Yi Min Laifi, Saboda Na Kama Ta Tana Cin Abinci Da Wani Gardi Da Muharraminta Ba, Cewar G-Fresh Al'Amin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *