
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar ADC a shekarar 2023 Dumebi Kachikwu ya caccaki su Atiku da suka shiga jam’iyyar su inda yace sune suka lalata Najeriya.
Yace ko da shugaban jam’iyyar da a jiya yace ya sauka daga mukaminsa dan a canja fasalin shugabancin jam’iyyar, Nwosu dama tun a shekarar 2022 wa’adin mulkinsa ya kare kuma suna kotu.
Yace Su Atiku lokacinsu yayi da ya kamata su koma gefe su baiwa matasa dama su mulki kasarnan.
A jiya ne dai gamayyar ‘yan Adawa suka taru suka bayyana aniyarsu ta tsayawa takara a karkashin jam’iyyar ADC.