Friday, December 5
Shadow

Rashin Adalci Ne A Bawa Ƴan Kwallo Milyan 150, Da Gidaje Kowannen Su Cikin Wata Ɗaya, Amma Ɗan Sanda Ya Shekara 35 A Ba Shi Milyan Biyu, Inji Sowore

Rashin Adalci Ne A Bawa Ƴan Kwallo Milyan 150, Da Gidaje Kowannen Su Cikin Wata Ɗaya, Amma Ɗan Sanda Ya Shekara 35 A Ba Shi Milyan Biyu, Inji Sowore.

Daga Muhammad Kwairi Waziri

Omoyele Sowore, ɗan gwagwarmaya kuma mai kare haƙƙin ɗan adam, ya bayyana rashin adalci a tsarin albashi da lada a Najeriya, yana mai cewa abin takaici ne yadda ake fifita ‘yan wasa fiye da ma’aikatan tsaro.

A cewarsa: “Rashin adalci ne tsantsa, ‘yan kwallo su yi wasa a cikin wata ɗaya a ba su Naira miliyan 150 da gidaje kowanne, amma ɗan sanda ya shekara 35 yana aiki ya samu Naira miliyan 2 kawai ba tare da wani tausayi ba.”

Karanta Wannan  Masu karamin karfi zamu sayarwa gidaje 753 da muka kwace daga hannun Emefiele a farashi me sauki>>Gwamnatin Tarayya

Sowore ya ce irin wannan bambanci yana nuna rashin daraja da ƙasa ke yi wa waɗanda ke sadaukar da rayukansu don tabbatar da tsaro da zaman lafiya. Ya bukaci a sake duba tsarin biyan haƙƙin ma’aikata a ƙasar.

Me zaku ce?

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *