Friday, December 5
Shadow

Sabuwar Baraka ta kunno kai a jam’iyyar ADC, Ana zargin Atiku da saye duk wani me fada aji a jam’iyyar da kudi, Peter Obi ya koka da cewa an mayar dashi saniyar ware

Rahotanni daga jam’iyyar ADC na cewa ana zargin Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar da saye duk wani me fada a ji a jam’iyyar da kudi.

Rahoton na jaridar Punchng yace duk sun koma abinda Atiku yake so shi ake yi a jam’iyyar.

Wasu masana harkar jam’iyyar ne suka sanar da jaridar wannan batu amma sun ce kada a fadi sunayensu dan kada a hukutasu.

Saidai me magana da yawun jam’iyyar ta ADC, Bolaji Abdullahi ya musanta wannan zargi inda yace za’awa kowa adalci a jam’iyyar.

Kuma abinda ke gabansu a yanzu shine kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu zabe a shekarar 2027.

Hakan na zuwane bayan da shugaban magoya bayan Peter Obi, Tanko Yunusa ya koka da cewa ba’a yi dasu an mayar dasu saniyar ware a jam’iyyar ADC.

Karanta Wannan  Ɗansanda ya sha barasa ya saki mutum 13 da ke tsare

A baya dai an rika rade-radin cewa, Peter Obi zai bar jam’iyyar ADC.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *