Friday, December 5
Shadow

Idan ADC ta tsayar dani takara babu shakka zan kayar da Shugaba Tinubu zabe a 2027>>Rotimi Amaechi

Tsohon Ministan sufuri, Rotimi Amaechi ya bayyana cewa, idan jam’iyyar ADC ta bashi takarar shugaban kasa a zaben 2027 tabbas zai kayar da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu

Ya bayyana hakane a kafarsa ta X.

Zan canja kundin tsarin mulki, zan kawo ƙarshen cin hanci cikin wata idan na zama shugaban ƙasa – Amaechi

Tsohon Ministan Sufurin Najeriya Rotimi Amaechi ya jaddada cewa zai canja kundin tsarin mulkin Najeriya idan aka zaɓe shi a matsayin shugaban ƙasa a shekarar 2027.

Amaechi ya bayyana haka a lokacin da yake jawabi a shafin sa na X a ranar Juma’a, inda yace zai kawo karshen matsalar cin hanci a cikin wata daya ko ya sauka daga mulki.

Karanta Wannan  Duk rintsi muna tare da Kashim Shettima>>Rahama Sadau bayan dambarwar data faru inda Ganduje ya kira sunan shugaba Tinubu ba tare da kiran sunan Kashim Shettima ba

Amaechi ya kuma bayyana Farfesa Mahmood Yakubu a matsayin lalataccen shugaban hukumar zaɓe a tarihin Najeriya.

Daga Usman Salisu

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *