Friday, December 5
Shadow

Muna Magana da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aiki yi a wadannan kasashe>>Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, suna aiki tare da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aikin yi a wadannan kasashe.

Ministan Gwadago, Muhammad Dingyadi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja.

Yace suna horas da matasan wanda zasu je wadannan kasashe su yi aiki kuma abin ya amfane su da kasa baki daya.

Ministan yace yanzu haka suna magana da daya daga cikin kasashen kuma sauran kasashen ma zasu ci gaba da neman wa matasan aikin a can.

Karanta Wannan  Ya kamata mutane su shiga taitayinsu su daina yada karya da bata sunan dan shugaban kasa, Seyi Tinubu>>Kungiyar Kiristoci ta CAN ta yi gargadi

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *