Friday, July 17
Shadow

Muna Magana da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aiki yi a wadannan kasashe>>Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin tarayya ta sanar da cewa, suna aiki tare da kasashen Saudiyya, Amurka, Ingila da sauransu dan samarwa matasa aikin yi a wadannan kasashe.

Ministan Gwadago, Muhammad Dingyadi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Abuja.

Yace suna horas da matasan wanda zasu je wadannan kasashe su yi aiki kuma abin ya amfane su da kasa baki daya.

Ministan yace yanzu haka suna magana da daya daga cikin kasashen kuma sauran kasashen ma zasu ci gaba da neman wa matasan aikin a can.

Karanta Wannan  Shuwagabannin tsaron Najeriya na shan suka bayan kìsàn mutane 250 a cikin makonni 2, ana zargin sun gaza

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *