Friday, January 23
Shadow

Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa da ake shirin yi.

Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida ne ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai.

Yace karin harajin kaso 5 akan kamfanonin sadarwar yana kunshene a cikin sabon kudirin dokar da majalisa ta amince dashi.

Yace yana wajan aka kawowa shugaba Tinubu maganar karin amma yace ba zai kara saka ‘yan Najeriya a cikin matsala ba.

Yace a baya an dakatar da karinne amma yanzu an cireshi gaba daya.

Karanta Wannan  Mun fi kowacce ƙungiya ƙoƙari a gasar zakarun turai - Kocin Arsenal

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *