Friday, December 5
Shadow

Da Duminsa: Bayan Kiraye-Kiraye, Gwamnatin Tarayya ta saka Asibitin Aminu Kano cikin wadanda aka yi ragin wankin Koda daga Naira dubu 50 zuwa Naira Dubu 12

Zuwa yanzu dai an saka Asibitin Malam Aminu Kano dake Kano cikin asibitocin gwamnatin tarayya ta aka yi ragin wankin Koda daga Naira dubu 50 zuwa Naira dubu 12.

A baya dai an samu suka ga gwamnati bayan data sanar da ragin kudin wankin kodar a asibitocin Gwamnatin tarayya ba tare da hadawa da asibitin malam Aminu Kano ba.

Lamarin ya jawo cece-kuce sosai musamman a kafafen sada zumunta.

Saidai a cewar tsohon Hadimin Gwamnan Kano, Abubakar Aminu Ibrahim ya bayyana cewa, yanzu an saka Asibitin malam Aminu Kano cikin wadanda akawa ragin.

Karanta Wannan  Akwai ƴanƙasar waje da ke kai hari a Benue - Alia

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *