Friday, December 5
Shadow

Ji Yanda ‘yansanda suka yi ta maza suka kashe Habu Dan Damisa duk da kokarin hanasu da wasu masu kumbar susa suka yi

Rahotanni sun bayyana cewa, Habu Dan Damisa da aka kashe ya mutu ne a hannun ‘yansanda.

Habu Dan Damisa sanannen dan daba ne dake kashe mutane da yi musu zalinci kala-kala amma saboda ana ganin yana da daurin gindi a wajan wasu ‘yan siyasa yasa yaki tabuwa.

Mutuwarsa ta zowa mutane da yawa da mamaki musamman jin cewa, a hannun ‘yansandan ya mutu.

Rahotanni sunce an yi kokarin hana ‘yansanda kashe Dan Damisa amma suka ki sauraren wannan kiraye-kirayen musamman la’akari da irin barnar da yake yi a cikin al’umma suka aikashi lahira.

Karanta Wannan  NNPP ta nemi afuwar Tinubu kan kalaman suka da ake zargin Kwankwaso ya yi masa

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *