Friday, December 5
Shadow

Alfashar dake faruwa a yankin Arewa ta zarce duk inda ake Tunani, Wai a Arewa ne za’a kama mutum da mata 3 a dakin Otal ya Rhasu>>Inji Sheikh Dr. Ahmad Gumi

Malamin Addinin Islama, Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya bayyana takaici kan yanda yanayin lalacewar tarbiyya musamman da yawaitar zinace-zinace suka yi yawa a tsakanin al’umma.

Malam ya bayyana hakane a yayin wa’azin da ya gudanar na Mukhtasar Khalil a masallacin Sultan Bello dake Kaduna Ranar Juma’a.

Malam yace Al’ummar Arewa da aka santa da Kunya da kawaici Yau Tiktok yasa mata sun zama marasa kunya.

Malam yace a Arewa ne aka samu wata mace tace Minista ya mata ciki ya kuma ki daukar nauyin dan.

Yace hakanan a Arewa ne aka samu wani ma’aikacin Kwastam da mata 3 a dakin Otal ya mutu.

Yace dole Allah ya jarrabemu.

Karanta Wannan  HOTUNA: A karon farko, Sarki Sanusi ya yi hawan Fanisau ba a doki ba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *