Friday, December 5
Shadow

Wahalar da ‘yan Najeriya suka shiga bayan da aka cire tallafin man fetur ba itace abin dubawa ba, Abinda ya kamata ya damemu shine abinda zai faru da ba’a cire tallafin man fetur din ba>>Inji Sarkin Kano, Muhammad Sanusi II

Me martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II ya bayyana cewa dama ba abin mamaki bane dan an samu hauhawar farashin kayan abinci da tsadar rayuwa bayan cire tallafin man fetur.

Yace dama hakan dole zata faru.

Yace babban abin dubawa shine abinda zai faru da ba’a cire tallafin man fetur din ba.

Ya bayyana hakane a wajan wani taro inda jawabinsa na wajan taron ke ta yaduwa a kafafen sadarwa.

Yace bashi ake ciyowa ana biyan kudin tallafin sanan akwai kudin ruwa da ake biya akan bashin.

Da yake magana kan irin shuwagabannin da ake dasu a Najeriya, yace yana mamakin ace mutum me ilimi amma ya zama da koron siyasa, hakanan yana mamakin shugaba da ba zai saurari suka daga na kusa dashi ba dan ya gyara inda yake da matsala.

Karanta Wannan  Wike Yace Hadakar ADC bata da Amfani inda yayi kira ga 'yan Najeriya su yi watsi da ita

Sarki Sanusi yace ko da an cire ‘yan majalisar Najeriya aka sake zuba wasu, ba lallai a ga canji ba, saboda gasunan da ilimi amma suna irin abubuwan Jahilai.

@msd__142

“They turned to praise Singers & illiterates” Emir of Kano Muhammad Sanusi ll hit Ministers

♬ original sound – Kabiru Msd

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *