
Bayan da Kasar Amurka ta farawa Najeriya katsalandan akan harkar tsaro da sunan ana yiwa Kiristoci Khisan Kiyashi, Har shugaban kasar Trump yayi barazanar kawo hari, Mutane na ta tunanin abinda Kasar ke son cimmawa a Najeriya.
Wani bature wanda wakili ne a kungiyar NATO, Gunther Fehlinger-Jahn ya bayyana cewa, Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu na kokarin ganin ya yi fafutuka da hada kan kasarsa amma Najeriya bata amfanar kowa da kowa.
Yace dan haka raba kasar shine Mafita.
Da yawa dai sun bayyana mamaki da jin wannan magana da ta fito daga bakin wannan bature inda Kiristoci da yawa ke fadar cewa ba abinda suke nema kenan ba.