Friday, December 5
Shadow

Muna baiwa shugaba Tinubu da sauran ‘yan Najeriya hakuri saboda munsan mun baku kunya, sau biyu kenan Super Eagles na kasa zuwa gasar cin kofin Duniya>>Inji Hukumar kwallon Najeriya, NFF

Hukumar kwallon kafa ta Najeriya, NFF tace tana baiwa shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da sauran ‘yan Najeriya hakuri saboda fitar da Super Eagles da kasar Dr. Congo ta yi a wasan neman cancantar zuwa buga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2026.

NFF tace lamarin abin takaicine matuka domin sau biyu kenan a jere tana kasa zuwa gasar.

Tace abin kunya ne amma tana neman afuwa.

Kasar Dr. Congo tawa Najeriya ci 4-3 bayan an tashi 1-1 a jiya Lahadi wanda hakan ya hana Najeriya damar kaiwa ga gasar cin kofin Duniya na shekarar 2026.

Karanta Wannan  Da Duminsa: Ji Matakin da aka dauka kan Sheikh Abduljabbar Bayan zaman Kwamitin Shura da Malam Lawal Triumph

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *