Friday, December 5
Shadow

An sake dawukye Dalibai a jihar Naija, Gwamnatin jihar Naija ta tabbatar da hakan saidai tace laifin hukumomin makarantar ne dan Gwamnati ta samu Rahoton hakan zai iya faruwa tace a kulle makarantu

Rahotanni daga jihar Naija na cewa, an sake yin garkuwa da dalibai na makatanta.

An sace daliban makarantar St. Mary’s School ce dake Papiri a karamar hukumar Agwara dake jihar ta Naija.

Daily Trust tace lamarin ya farune da misalin karfe 2 zuwa 3 na dare.

Zuwa yanzu dai ba’a san yawan daliban da aka sace ba.

Me magana da yawun gwamnatin jihar Naija, Abubakar Usman ya tabbatar da wannan labari inda yace ana kokarin kubutar da daliban.

Saidai ya dora laifin faruwar hakan akan hukumomin makarantar inda yace Gwamnati ta samu rahoton cewa, hakan zai iya faruwa.

Kuma ta bayar da sanarwa cewa, a kulle duka makarantu a yankin saidai wannan makaranta taki jin wannan shawara inda suka ci gaba da karatu.

Karanta Wannan  Babu maganar tattaunawa, ba zamu rage ko sisi a karin kudin kiran da muka yi ba>>Kamfanonin Sadarwa Irin su MTN, Airtel suka bayyana

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *