Friday, December 5
Shadow

Yayin da Dalibai Kiristoci ke zargin an hanasu gona coci a jami’o’in Kashere, Gombe dana BUK, Kano, Shima wani dalibi musulmi yayi zargin cewa an hana Musulmai gina masallaci a jami’ar Jos, UniJos

A dazu ne hutudole ya kawo muku rahoton yanda wasu Kiristoci dalibai daga jami’o’in BUK, Kano da Kashere, Gombe inda suke zargin an hanasu gina coci a wadannan makarantu yayin da aka bar musulmai suka gina masallatai.

A martani ga wannan zargi shima wani dalibi musulmi yai zargin cewa an hana dalibai musulmai gina masallaci a jami’ar UNIJos, dake jihar Filato.

Yace duk da akwai masalacin da aka fara ginawa amma an hana a karasashi.

Sannan yayi zargin cewa an ma hana musulmai yin salla a masallacin da ba’a karasa ba.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo:Ina son aure, idan na samu wanda ke sona ima ina sonshi, zan yi Aure>>Inji Tauraruwar fina-finan Hausa, Firdausi Yahya

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *