Wednesday, April 8
Shadow

Da Duminsa: Shugaba Tinubu ya aikawa majalisar Dattijai da sunan Janar Christopher Musa su tantanceshi a matsayin Minista tsaro

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya aika da sunan Janar Christopher Musa ga majalisar Dattijai dan su tantanceshi a matsayin ministan tsaro.

A cikin wasikar da shugaba Tinubu ya aikawa kakakin majalisar Dattijai Godswill Akpabio ya bayyana cewa yana son janar Christopher Musa ya maye gurbin Muhammad Abubakar Badaru a matsayin Ministan tsaro.

A jiya litinin ne dai Muhammad Badaru Abubakar ya ajiye mukaminsa a matsayin Ministan tsaro inda ya ce baya jin dadi.

Janar Christopher Musa na da shekaru 58 a Duniya kuma ya nuna bajinta a aikin soja sosai inda ya samu kyautukan karramawa da yawa.

Karanta Wannan  Wallahi Duk Mai Sona Da Gaske Ya Zo Ya Biya Sadaki Kawai, Na Yafe Lefe, Domin Ina Da Kayan Sawa, Biyo Ka Kawai Zan Yi, Saboda Ji Nàķe Kamar Na Fi Kowàcè Maçe Bukataŕ Àùrè, Inji Faizat Abubakar

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *