Tuesday, December 16
Shadow

Da Duminsa: EFCC sun sake kama Tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami

Rahotanni daga Abuja na cewa hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun sake kama tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami.

Sahara Reporters sun ruwaito cewa EFCC sun kama Abubakar Malami ne da yammacin jiya, Latinin.

Sannan yanzu haka yana ta kokarin ganin ya samu manyan sakatarorin gwamnati 2 ne da zasu tsaya masa a bayar da belinsa.

Ana zargin Malami ne da aikata ba daidai ba da kudaden da aka kwato na tsohon shugaban kasa, Marigayi janar Sani Abacha.

Zargin da Malami ya dade da karyatawa.

Karanta Wannan  Kalli yanda Wata mamakon Gobara da ba'a san daga inda ta taso ba ta barke a kasar Israyla tana ta yaduwa sosai

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *