Saturday, September 12
Shadow

Da Duminsa: EFCC sun kulle gidan da matar Malami, Diyar Tsohon shugaban kasa take ciki

Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumar yaki da rashawa da cin hanci, EFCC sun kulle gidan tsohon Ministan shari’a, Abubakar Malami inda matarsa, diyar tsohon shugaban kasa, Fatima Buhari take.

Jam’iyyar ADC ce ta bayyana hakan inda ta zargi Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu da wulakanta Buhari ta wannan hanya.

Ana zargin Malami da Almundahanar kudade da yawa ciki hadda kudaden Abacha da aka kwato daga kasashen waje.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Matashi Garba Maiwada ya zargi Gwamna Zulum da yin dama-dama da Maiduguri ta yanda matasa sai tafiya ci rani suke saboda ba aikin yi a garin

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *