Saturday, December 27
Shadow

Biyo bayan shawarar da Dr. Ahmad Gumi ya bayar, Gwamnatin tarayya tace ta fara magana da kasar Turkiyya dan su taimakawa Najeriya magance matsalar tsaro

Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya bayyana cewa, sun tuntubi kasar Turkiyya dan ta taimakawa Najeriya wajan magance matsalar tsaro.

Ya bayyana hakane yayin ganawa da kungiyar Kiristoci ta CAN a ziyarar data kai masa a fadarsa dake Abuja.

Shugaban yace akwai bukatar Kiristoci su taya Najeriya da Addu’a dan kawo karshen matsalar.

Ya kuma kara da cewa, sun siyi Jiragen yaki 3 daga kasar Amurka amma ba zasu zo da wuri ba.

Hakan na zuwane bayan da Sheikh Dr. Ahmad Gumi ya baiwa Gwamnatin tarayya shawarar ta yi watsi da kasar Amurka ta koma neman taimakon tsaro daga kasashen China, Pakistan da Turkiyya.

Karanta Wannan  Kalli Bidiyo: Yanzu mun gano cewa Tinubu baya kishin Addini, Baya sauraren mu, Muna fatan Allah ya saukeshi karya kara shekara daya akan Mulki>>Inji Malaman da suka tallata Tinubu a 2023

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *