
Tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana cewa, bashi da alaka ta kusa da shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu.
Yace abinda ya faru shine, ko a 2023 da ya goyi bayan Tinubu, wasu malaman addinin musulunci ne daga jihohin Yarbawa suka sameshi suka rokeshi akan ya goyi bayan Tinubu.