
Rahotanni sun tabbatar da cewa, Gwamnatin tarayya ta shigar da malam Nasiru Ahmad El-Rufai kara kotu.
Gwamnatin ta shigar da Malam Nasiru Ahmad El-Rufai kotu ne bisa zargin maganar da yayi ta cewa yana sauraren duk wayar da me baiwa shugaban kasa shawara kan harkar tsaro, Malam Nuhu Ribadu ke yi.
Malam Nasiru Ahmad El-Rufai ya bayyana hakane a wata hira da aka yi dashi a Arise TV.
Shahararren lauya, Deji Adeyanju ne ya wallafa takardar shigar da karar a shafinsa na X.
