
Rahotanni sun bayyana cewa, Hukumomin Najeriya sun kori dan kasar Amirkar nan me suna Mr. Alex Barbir wanda ya shigo Najeriya yake tunxura Kiristoci akan Musulmai.
Malam Bashir Ahmad wanda tsohon Hadimin shugaban kasa ne ya bayyana hakan ta shafisa na X inda yace wata majiya me karfi ta sanar dashi hakan.
A baya dai, an yi kiran Hukumomin su dauki mataki akan wannan bature da ba’a amince da salon da ya shigo dashi Najeriya ba.