
Hukumar zabe me zaman kanta, INEC ta sanar da cire shugaban jam’iyyar ADC na rikon kwarya, David Umahi da sakataren jam’iyyar na rikon kwarya, Rauf Aregbesola daga shafinta na tattara bayanan shuwagabannin jam’iyyun Najeriya.
INEC tace ta yi hakanne saboda karar da aka shigar a kotun daukaka kara daga wani bangare na jam’iyyar da basu yadda da shugabancin su David Mark ba.
Kwamishinan yada labarai na INEC, Mohammed Kudu Haruna ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar, yace zasu dakata har sai sun ji hukuncin da kotun daukaka karar zata yanke.
Wanda ya shigar da karar shine Nafiu Bala Gombe wanda ke ikirarin cewa shine shugaban jam’iyyar ta ADC.