
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya sauke Ministan Kudi, Wale Edun da Ministan Gidaje Da ci gaban birane Umar Dangiwa.
Sakataren Gwamnati, Sanata George Akume ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar.
An baiwa Wale Edun umarnin ya mikawa karamin Ministan kudi, Mr. Taiwo Oyedele ragamar ma’aikatar.
Hakanan shugaba Tinubu ya nada Mr. Muttaqha Rabe Darma (PhD) a matsayin Ministan Gidaje da ci gaban birane.