
Rahotanni sun bayyana cewa, matatar man fetur ta Dangote zata fara hako danyen man fetur.
Mataimakin Dangote, Devakumar Edwin ne ya bayyana hakan a wata ganawa da aka yi dashi inda yace har sun fara gwajin hako man fetur din.
Yace Hakowar ta Gwaji zata dauki akalla zuwa Sati 3 ko 4.
Yace daga nan kuma zasu fara hako man sosai ta yanda zasu rika sayar dashi ko amfani.