
Wata matashiya me suna Fatima Aslam ta dauki hankula sosai a kafafen sadarwa bayan bayyana cewa ta bar Musulunci.
Matashiyar tace satinta Biyu kenan da barin addinin Addinin Musulunci.
Tace ‘yan uwanta da abokan arziki sai kiran wayarta suke amma ba zata koma addinin musulunci ba.
Ta kara da cewa, ta ma daina saka Hijabi.
Lamarinta ya jawo cece-kuce da daukar hankula.
