
Wani shugaban ‘yansanda a kasar Congo ya dauki hankula a kafafen sada zumunta bayan da aka ganshi ya yanke jiki ya fadi a yayin da yake tsaka da yiwa jami’an sa jawabi.
Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya farune saboda mankas yake da giya.
Daga baya dai an ga jami’an nasa sun je sun kamashi sun tayar dashi tsaye.