
Rikici ya barke tsakanin Rahama Saidu me babban shago da yaran shagonta 3.
Rahama Ta zargi yaran shagon da yi mata sata.
Tace abaya 2 suka sace mata.
Ta wallafa Sunayensu a shafinta na sada zumunta inda tace yanzu basa aiki da ita.
A baya ta wallafa hadda hotuna da Bidiyon su kamar yanda suka yi zargi amma ta goge.
Saidai daya daga cikin wadanda ta kora daga aikin, ta fito ta musanta wannan zargi.
Tace abaya da tace sun bata sayarwa suka yi kuma an turawa Rahama kudinsu a asusun bankinta.
Ta yi zargin cewa, Sun bayyana wa Rahama Saidu cewa ba zasu iya ci gaba da aiki da ita ba saboda albashin da take basu yayi kadan
Shine ta fito da hanyar yi musu sharri.
Ta kuma ce tana bin Rahama Saidu Albashin watanni 2 bata biyata ba.