Monday, May 19
Shadow

Kotu ta hana CBN baiwa jihar Rivers rabonta na kudaden shiga daga gwamnatin tarayya

Babbar Kotun gwamnatin tarayya dake Abuja ta hana babban bankin Najeriya, CBN ci gaba da turawa jihar Rivers kudadenta na shiga da gwamnatin tarayya ke aikawa kowace jiha.

Mai Shari’a, Joyce Abdulmalik ce ta yanke wannan hukunci bisa dalilin cewa gwamnan jihar Sim Fubara baya bin doka wajan kashe kudaden da ake turawa jihar.

Dan hakane tace kada a sake turawa jihar wadannan kudade.

Wasu masu sharhi da yawa dai sun bayyana wannan mataki da cewa ba ya rasa nasaba da rashin jituwa dake tsakanin Gwamna Sim Fubara da Nyesome Wike.

Karanta Wannan  Daya daga cikin matan da mutuminnan na kasar Equatorial Guinea yayi lalata dasu kuma Bidiyon lalatar ya bayyana ta kàshè kanta

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *