Wednesday, May 13
Shadow

Shugaban ‘Yansandan Najeriya ya bayar da umarni ga ‘yansanda su daura bakin kyalle dan nuna Alhinin rayuwar shugaban sojoji

Shugaban ‘yansandan Najeriya, IGP Kayode ya bayar da umarni ga ‘yansandan kasarnan da su daura bakin kyalle na tsawon kwanaki 7 dan nuna alhinin rasuwar shugaban sojoji Lt. Gen. Taoreed Lagbaja.

Kakakin ‘yansandan Najeriya, ACP Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana haka a wata sanarwa da ya fitar ga manema labarai.

Yace wannan matakine da aka dauka dan girmama tsohon shugaban sojojin da kokarin da ya nuna wajan yaki da matsalar tsaro.

Karanta Wannan  Mahaifina ya cika kwanaki 40 da rigamu gidan gaskiya>>Rahama Sadau

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *