Friday, December 5
Shadow

Kalli Bidiyo da hotuna yanda motar Dangote ta buge mutane 3 suka mùtù a Jihar Legas

Hukumar kula da ababen hawa ta jihar Legas, LASTMA ta tabbatar da mutuwar mutane 3 bayan da motar Dangote ta bugesu.

Rahoton Daily Post yace motar Dangoten dake tafiya akan titin Ita-Opo, Epe ta samu matsalar birki ne inda hakan yasa ta yi taho mu gama da wasu motocin.

Shugaban hukumar ta LASTMA, Olalekan Bakare-Oki ya tabbatar da faruwar lamarin ta bakin kakakin hukumar Taofiq Adebayo, yace motar ta Dangote ta buge Keke Napep da wata mota dake ajiye a gefe.

Karanta Wannan  Na sake fada cewa bani da lokacin da zan roki Allah ya bani miji>>Matashiya ta sake nanatawa

Yace direban keke Napep din da dalibai biyu daga makarantar Manpower Technical School sun mutu sanadiyyar hadarin

Karanta Wannan  Ji bayani Dalla-Dalla: DA KYAR JAMI'AN TSARO SUKA KWACI MADAGWAL A HANNUN MABIYA KWANKWASIYYA DUK KUWA DA CEWA YA TUBA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *