
Ƙungiyoyin ma’aikatan manyan makarantun Najeriya na ci gaba da yin watsi da sabon shirin da gwamnatin tarayyar kasar ta ɓullo da shi domin inganta jin dadin ma’aikata, da haɓaka ƙwarewar aiki, ga ma’aikatan manyan makarantun ƙasar.
Ita dai gwamnatin Najeriyan ta ƙaddamar da wani sabon shiri wanda aka tsara zai bayar da bashin kudi har naira miliyan 10 ga ma’aikatan manyan makarantun ƙasar da suka haɗa da na jami’a da kwalejin kimiyya da fasaha da kuma kwalejin ilimi.
To sai dai ƙungiyoyin ma’aikatan na ganin cewa ba hanyoyin samar da bashi gare su ya kamata gwamnatin ta ɓullo da su ba a wannan lokaci da ake ciki.