Thursday, July 16
Shadow

A yau ko Gobe zamu biya Super Eagles hakokinsu>>Inji Gwamnatin tarayya

Bayan da Kungiyar kwallon kafar Najeriya, Super Eagles suka fito suka ce ba zasu buga wasan Algeria a gasar AFCON da ake bugawa a kasar Morocco ba saboda hakkokinsu da ba’a biya ba.

Gwamnatin tarayya tace an shirya tsaf dan biyan hakkokin na ‘yan wasan kuma zasu ya fara ganin Alert yau ko gobe.

Karamar Ministar kudi, Doris Nkiruka Uzoka Anite ce ta bayyana hakan a sanarwar data fitar.

Tace CBN ya fitar da kudin kuma an canjasu zuwa dala za’a Turawa kowane dan wasa zuwa Asusunsa na banki na Dala.

Karanta Wannan  Yanzu dole zamu sa ido akanka tunda kana barzanar kwace mana mulki>>Gwamnatin Tinubu ga El-Rufai bayan da ya canja Jam'iyya daga APC zuwa SDP

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *