Thursday, February 5
Shadow

A zaben 2027 ba zamu saki baki a mana abinda aka ga dama ba>>Atiku Abubakar ya bayyana shirin cin zabe na musamman da yake yi

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP a zaben shekarar 2027, Alhaji Atiku Abubakar ya bayyana cewa zaben 2027 ba zai zama kamar sauran zabukan da aka yi a baya ba.

Yace ‘yan adawa na hadaka ta musamman dan ganin sun yi nasara akan gwamnati me ci saboda tsare-tsaren gwamnatin basu kawowa kasar ci gaba ba.

Ya bayyana hakane a Abuja ranar Talata a yayin ziyarar da wasu ‘yan masana’antar fina-finan Hausa ta Kannywood suka kai masa.

Kungiyar tace tana tare da Atiku a zabe me zuwa.

Wani dan siyasa daga jihar Zamfara, Dr. Aslam Aliyu ne yawa kungiyar jagora zuwa wajan Atiku.

Karanta Wannan  'Yan kasar Afrika ta kudu na ta murna bayan kashe 'yan Najeriya 6

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *