Friday, June 26
Shadow

An fara Magudun zaben shekarar 2027>>Atiku Abubakar ya koka

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Alhaji Atiku Abubakar ya koka da cewa, an fara magudin zaben shekarar 2027.

Ya bayyana hakan a shafinsa na sada zumunta inda yace an fara hakannne ta hanyar kaucewa gyaran dokar zabe.

Ya zargi majalisar tarayya da kaucewa gyara dokar zabe wadda zata sa kada a maimaita kuskuren da aka tafka a zaben shekarar 2023.

Atiku yace idan ba’a gyara dokar zaben ba ba lallai a samu sakamakon zabe sahihi a zaben shekarar 2027 ba.

Karanta Wannan  Gwamnati ta karyata Lauyanta inda tace duka wadanda aka kama kananan yarane kuma za'a binciki jami'an tsaron da suka kamasu dan yi musu hukunci

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *