
Rahotanni sun bayyana cewa, an kama tsaffin shuwagabannin matatun man fetur da aka sauke satin daya gabata saboda zargin sace kudaden da aka ware dan gyaran mamatun man fetur din.
Matatun man fetur din sune Warri, Fatakwal da Kaduna.
Jimullar kudaden da ake zarginsu da sacewa sun kai Dala $2,956,872,622.36.
A matatar man fetur ta Fatakwal ana neman dala $1,559,239,084.36 a yayin da a matatar man fetur ta Kaduna ana neman dala $740,669,600 inda a matatar man Warri ana neman dala $656,963,938.
Hakanan wata Majiya tace an samu Naira Biliyan 80 a asusun daya daga cikin manyan ma’aikatan.
Ana dai zargin wadannan shuwagabannin da yaudarar ‘yan Najeriya musamman game da gyaran matatar man Warri.