Saturday, December 13
Shadow

An yankewa malamin jami’a hukuncin daurin rai da rai bayan samunsa da yiwa dalibarsa Fyàdè

Wata kotun musamman dake kula da rikice-rikicen cikin gida dake Ikeja jihar Legas ta yankewa wani malami a kwalejin ilimi ta Adeniran Ogunsanya College of Educatio daurin rai da rai bayan samunsa da laifin yiwa dalibarsa fyade.

Malamin me suna Kolawole Muyiwa ya musanta zargin da ake masa bayan da aka gurfanar dashi a gaban kotun.

Ya aikata laifinne a ranar 11 ga wata October na shekarar 2021 a farfajiyar makarantar.

An gabatar da shaidu da suka hada ‘yansandan da suka yi bincike akan lamarin, da lauya da wadda akawa fyaden.

Mai shari’a, Justice Rahman Oshodi ya bayyana cewa, duka wadanda suka bayar da shaida akan lamarin labarinsu yayi daidai da wadda akawa fyaden dan haka aka yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Karanta Wannan  Game da hatsarin da Jarumi Adam A. Zango ya yi, bayanai na nuna an samu wasu marasa Imani sun sace masa wayar sa da kuɗin sa har da ɗan cincin ɗin da mahaifiyar sa tayi masa guzuri da shi da sauran abubuwan amfani

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *