
Babban dan siyasa daga jihar Kano, Alhaji Tanko Yakasai ya bayyana cewa, kuri’ar Arewa kadai ba zata saka dan takara ya ci zaben shugaban kasa ba.
Yace hakanan kuri’ar kudu kadai itama ba zata sa mutum ya ci zaben shugaban kasa ba.
Yace dole sai yankunan biyu sun hada kai sun kawo dan takara da ya ke da karbuwar da zata sa ya ci zabe, yace kuma dole dan takarar ya zamana yana da kudi.
Yace saboda zaben Najeriya dole sai da kudi ake cinsa.