
Kungiyar tuntuba ta Arewa me suna Arewa Consultative Forum ta bayyana cewa mutanen Arewa ne ke da kuri’un da zasu iya sanyawa dan takara ya zama shugaban kasa a shekarar 2027.
Shugaban kwamitin Amintattau na ACF, Alhaji Bashir M. Dalhatu ne ya bayyana hakan inda yace suna ta samun bukatar su saka ido dan gano dan takarar da ke da ayyukan da zai amfanar da Arewa a shekarar 2027 dan a Zabeshu.
Saidai yace abinda yafi damunsu a yanzu matsalar tsaro ce inda yace suna kira ga gwamnati da ta magance matsalar kamin lokaci ya kure mata.