Friday, May 23
Shadow

Author: Auwal Abubakar

An koro ‘yan Arewa 114 guda daga jihar Ondo

An koro ‘yan Arewa 114 guda daga jihar Ondo

Duk Labarai
Gwamnatin jihar Ondo dake kudancin Najeriya ta kamo 'yan Arewa su 114 da aka samu a dazukan jihar inda aka dawo dasu gida Arewa. Hukumar jami'an tsaron Amotekun na jihar ne suka kama mutanen suka kuma taso keyarsu zuwa Arewa. Kwamandan Amotekun din, Akogun Adetunji Adeleye ya bayyana cewa sun kama mutanen ne saboda sun tambayesu me ya kawosu dajin jihar amma in banda mutum uku a cikinsu, duka sun kasa fadin abinda ya kaisu jihar. Ya kara da cewa, wadanda suka kaisu dazukan jihar a manyan motoci sun ce musu su bazama a daji ne nan gaba zasu sanar dasu abinda zasu yi. Ya kara da cewa, Gwamnan jihar, Hon. Lucky Orimisan Aiyedatiwa ya basu umarnin kama mutanen da mayar dasu Arewa. Yace, tabbas kundin tsarin mulkin Najeriya ya baiwa kowa damar yin walwala da zuwa inda yake so a f...
Dattijo Edwin Clark ya rasu yana da shekara 97

Dattijo Edwin Clark ya rasu yana da shekara 97

Duk Labarai
Dattijo a yankin Neja Delta da ke kudancin Najeriya kuma tsohon kwamashina, Edwin Clark, ya rasu yana da shekara 97 da haihuwa. A cewar wata sanarwa da kafofin yaɗa labarai a Najeriya suka ruwaito daga iyalinsa, tsohon shugaban ƙungiyar rajin kare yankin Neja Delta ta Pan Niger Delta Forum (PANDEF) ya rasu ranar Litinin da dare. "Mutumin da aka haifa a Kiagbodo da ke yankin Ijaw na jihar Delta, Clark ya yi aiki tare da gwamnan mulkin soja Samuel Ogbemudia, da Janar Yakubu Gowon tsakanin shekarun 1966 zuwa 1975," a cewar sanarwar. Ya riƙe muƙamin kwamashinan yaɗa labarai a shekarar 1975.
An Kkàshè tsohon shugaban karamar hukuma da wasu mutane 6 Bayan da rikicin siyasa ya barke tsakanin APC da PDP

An Kkàshè tsohon shugaban karamar hukuma da wasu mutane 6 Bayan da rikicin siyasa ya barke tsakanin APC da PDP

Duk Labarai
Rahotanni daga jihar Osun na cewa, tsohon shugaban karamar hukumar Irewole, Mr. Aderemi Abbas da wasu mutane 6 sun mutu bayan da rikicin siyasa ya barke a jihar. Rikicin ya barkene bayan da kotu ta tabbatar da shuwagabannin kananan hukumomi da kansiloli na Jam'iyyar APC a matsayin wadanda suka lashe zabe a jihar. A baya dai,Gwamnan jihar, Ademola Adeleke ya kwarmata cewa minista Adegboyega Oyetola wanda tsohon gwamnan jihar ne na son tayar da rikici a jihar bosa goyon bayan jami'an tsaro. Rahoton jaridar Punchng ya bayyana cewa wani jami'in tsaro dake tsaye kusa da gawar Abbas ya bayyana cewa tsohon shugaban karamar hukumar ya mutu ne a yayin da rikici ya barke tsakanin 'yan siyasar. Rahoton yace a ranar Litinin an samu tashe-tashen hankula a kananan hukumomi daban-daban dake...
An kama malamar makaranta da laifin yiwa dalibinta me shekaru 17 fyade har ta dauki ciki

An kama malamar makaranta da laifin yiwa dalibinta me shekaru 17 fyade har ta dauki ciki

Duk Labarai
Wata malamar makaranta a garin Rochdale Shawnee Nicole Despain me shekaru 26 na fuskantar tuhuma bayan da aka sameta da laifin yiwa dalibinta me shekaru 17 fyade. Malamar na karantarwa ne a makarantar Rockdale High School dake jihar Texas ta kasar Amurka. Da farko dai ta musanta zargin. Saidai daga baya an gano sakonnin soyayyar da suka rika aikawa juna ita da dalibin nata hadda ma hotunansa tsirara a wayarta. Sannan ta boyewa mijinta bata gaya mai cewa cikin da take dauke dashi ba nashi bane na dalibinta ne sai da aka yi bincike aka gano hakan. Malamar dai zata iya fuskantar hukuncin daurin shekaru 20 a gidan yari amma a yayin yanke hukunci, Alkali ya yanke mata hukuncin daurin talala na shekaru 10 sannan an kwace lasisinta na aikin koyarwa.
Har yanzu Hukumar HISBAH ta Kano ta kasa kwato Shafinta na Facebook da aka mata kutse ana ta saka hotunan batsa

Har yanzu Hukumar HISBAH ta Kano ta kasa kwato Shafinta na Facebook da aka mata kutse ana ta saka hotunan batsa

Duk Labarai
Shafin Facebook na hukumar HISBAH ta Kano har yanzu yana hannun wani bata gari da ya musu kutse kuma yace saka hotunan batsa a kansa. Tun a watan Augusta na shekarar 2024 ne dai aka yiwa shafin kutse inda Hukumar HISBAH din ta rasa iko dashi, yanzu watanni 6 kenan. Shugaban HISBAH, Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya tabbatar da faruwar lamarin inda yace bangaren fasahar zamani na HISBAH suna kan kokarin dawo da shafin hannun hukumar. Saidai har yanzu shiru kake ji. Da Sahara Reporters suka tuntubi hukumar ta HISBAH tace har yanzu tana kan kokarin kwato shafin daga hannun bata garin da suke da iko dashi.
An kama mutane 2 da yiwa yarinya me shekaru 12 fyàd a jihar Yobe

An kama mutane 2 da yiwa yarinya me shekaru 12 fyàd a jihar Yobe

Duk Labarai
'Yansanda a jihar Yobe sun kama mutane 2 da ake zargin sun yiwa yarinya me shekaru 12 fyade a jihar. Lamarin ya farune a kauyen Jalingo dake karamar hukumar Tarmuwa ta jihar. Kakakin 'yansandan jihar, SP Dungus Abdulkarim ya tabbatar da faruwar lamarin a Damaturu ranar Litinin. Ya kara da cewa lamarin ya farune ranar 15 ga watan Fabrairu da misalin karfe 3:30 na rana inda wanda ake zargin suka ja yarinyar zuwa daji suka zakke mata. Ya kara da cewa, sun jiwa yarinyar ciwo inda aka kai ta Asibiti sannan kuma an kama wadanda ake zargin.
Dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya bayar da tallafin Naira Miliyan 100 ga dalibai a jihar Borno

Dan Shugaban kasa, Seyi Tinubu ya bayar da tallafin Naira Miliyan 100 ga dalibai a jihar Borno

Duk Labarai
Dan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu, Seyi Tinubu ya bayar da tallafin Naira Miliyan 100 ga dalibai da ambaliyar ruwa da aka yi a jihar Borno a watan Satumba na shekarar data gabata ya shafa. Dalibai daga makarantun gaba da sakandare 6 ne suka amfana da tallafin wanda ya hada da buhunan shinkafa, Taliya, Gishiri, Magi, Man Girki da sauransu. Da yake kaddamar da rabon tallafin, Seyi Tinubu yace ya bayar da tallafinne dan karfafa gwiwar daliban su koma da ci gaba da karatu a makarantunsu. Babban me baiwa shugaban kasar shawara akan harkar dalibai, Hon. Sunday Adebayo ne ya wakilci dan shugaban kasar inda yace gidauniyar NOELLA Foundation da Seyi Tinubu da abokansa ne suka bayar da tallafin. Ya kara da cewa an zabi daliban ne da lamarin yafi shafa kamin raba musu tallafin.
Shugaba Tinubu ya kashe Naira Biliyan 36 wajan Tafiye-Tafiye a shekarar 2024

Shugaba Tinubu ya kashe Naira Biliyan 36 wajan Tafiye-Tafiye a shekarar 2024

Duk Labarai
Gwamnatin shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ta a kashe Naira Biliyan 36.3 wajan tafiye-Tafiye a shekarar 2024 data gabata. Kafar Open Treasury Portal ce ta bayyana hakan a wasu bayanai data tattara inda tace shugaban ya kashe kudadenne wajan tafiye-Tafiye zuwa kasashen waje. Bayanan sunce idan aka hada da kudaden da shugaban kasar ya kashe a tafiye-Tafiyen da yayi na cikin gida, ya kashe jimullar Naira Biliyan 83 kenan. Yawan kudaden da shugaban ke kashewa wajan tafiye-Tafiyen sun sakawa 'yan Najeriya damuwa musamman ma lura da yanda gwamnati ke kukan karancin kudin gudanar da ayyuka. Peter Obi a kwanakin baya yayi kira ga shugaba Tinubu da ya rage yawan tafiye-Tafiyen da yake yi.