Monday, December 15
Shadow

Author: Bashir Ahmed

Dan majalisar dokoki na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya dauki hankula saboda nada masu taimaka masa guda 106

Dan majalisar dokoki na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya dauki hankula saboda nada masu taimaka masa guda 106

Duk Labarai
Dan majalisar wakilai na majalisar jihar Nasarawa, Musa Gude ya nada masu taimaka masa guda 106. Ya bayyana hakane a hirar da yayi da kamfanin dillancin labaran Najeriya, NAN inda yace ya nada mutane 106 a matsayin masu taimaka masa ne dan ya tallafawa rayuwarsu. Yace daga ciki akwai wadanda yake biya albashin Naira Dubu 10 har zuwa Dubu 100. Dan majalisar wanda a jam'iyyar SDP yake daga mazabar Uke/Karshi yace ya tallafawa mutane a bangarori daban-daban da suka hada da Noma, ilimi, da sauransu.
Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Zamu Tùbè kayan mu, mu yi Tumbur mu nuna komai mu yi zànga-zànga tsyrara idan ba a daina rushe mana gidaje ba>>Inji Matan Legas

Duk Labarai
Mata a birnin Legas sun yi barazanar yin zanga-zangar tsirara dan tursasa daina rushe musu gidaje. Matan daga yankin Ilaje sun yi zanga-zangar lumana zuwa majalisar dokokin jihar ta Legas inda suka nemi taimakon gwamnan jihar, Babajide Sonwo Olu da kakakin majalisar Dokokin jihar,Mudashiru Obasa su saka baki a daina rushe musu gidaje. Sun zargi sarakunan gargajiyarsu da yi musu kwacen gidaje. Daya daga cikin matan wadda dattijuwa ce, ta fito inda take barazanar cewa, zasu yi zanga-zanga tsirara idan ba a daina rushe musu gidaje ba. Shima shugaban mazauna yankin na Ilaje, Rafael Irowainu ya bayyana cewa wasu sarakuna na amfani da sunan shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu suna rushe gidaje dan su yi gine-gine. Ya kara da cewa, amma basu yadda shugaba ne ya aika mutanen ba.
Sai an kawo mana dauki, Lamuran tsaro sun ta’azzara>>Inji Gwamnan riko na jihar Katsina, wanda Gwamna Radda ya barwa jihar a hannunsa

Sai an kawo mana dauki, Lamuran tsaro sun ta’azzara>>Inji Gwamnan riko na jihar Katsina, wanda Gwamna Radda ya barwa jihar a hannunsa

Duk Labarai
Gwamnan riko na jihar Katsina wanda gwamna Dikko Radda ya barwa jihar a hannunsa Malam Faruk Lawal-Jobe ya yi kira ga gwamnatin tarayya data kawo musu dauki a jihar game da tabarbarewar lamuran tsaro. Wannan kira nasa na zuwane bayan harin da 'yan Bindiga suka kai unguwar Muntau dake garin Malunfashi a jihar Katsina suka kashe mutane akalla 13 dake sallar Asuba. Hakanan maharan sun rika harbin kan mai uwa da wabi inda kuma suka sace mutane 60, kamar yanda kafar Rariya ta tuwaito. Hakan na zuwane a yayin da Gwamna Dikko Radda ke kasashen Turawa nema Lafiya amma an hangoshi a wasu hotuna yana daukar hoton garin da yaje. Gwamnan rikon, Malam Faruk Lawal-Jobe ya nemi gwamnatin tarayya data kawowa jihar dauki lura da yanda lamuran tsaro suka tabarbare tare da neman Shugaban kasa ya ...
Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Ba zan iya sake jefa ‘yan Najeriya a wata sabuwar Wahala ba: Shugaba Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa

Duk Labarai
Shugaban kasa, Bola Ahmad Tinubu ya soke karin kaso 5 akan kamfanonin Sadarwa da ake shirin yi. Shugaban hukumar NCC, Aminu Maida ne ya bayyana hakan a yayin zantawa da manema labarai. Yace karin harajin kaso 5 akan kamfanonin sadarwar yana kunshene a cikin sabon kudirin dokar da majalisa ta amince dashi. Yace yana wajan aka kawowa shugaba Tinubu maganar karin amma yace ba zai kara saka 'yan Najeriya a cikin matsala ba. Yace a baya an dakatar da karinne amma yanzu an cireshi gaba daya.
Ina son shiga Aljannah>>Inji Shugaban kasar Amurka, Donald Trump

Ina son shiga Aljannah>>Inji Shugaban kasar Amurka, Donald Trump

Duk Labarai
Shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana son shiga Aljannah. Ya bayyana cewa dalili ma kenan da yake ta kokarin ganin ya kawo karshen yakin kasashen Russia da Ukraine. A baya Shugaba Trump ya gana da shugaban kasar Russia, Vladimir Putin sannan ya gana da shugaban kasar Ukràìnè sa shuwagabannin kasashen Turai. A nan gaba yace zai hada Putin da Zelenskyy su yi zaman sulhu. Tun kamin ya zama shugaban kasa yayi Alkawarin cewa idan ya ci zabe, zai tabbatar ya kawo karshen yakin.